📻
  • Sun, Mar 2026

Id hic soluta omnis et ratione. Voluptatibus itaque corrupti at error ut nulla. Beatae quasi sed odio incidunt voluptas impedit.

Ƙungiyar gwamnonin arewacin Najeriya ta yi Alla-wadai da kashe-kashen mutane a jihohin Katsina, Kwara da kuma Benue, inda suka kwatanta hakan a matsayin rashin imani kuma cin mutunci ga ƙasa.

Alla-wadai ɗin na zuwa ne bayan munanan hare-hare da aka kai karamar hukumar Kaiama na jihar Kwara, inda waɗanda ake kyautata zaton ƴanbindiga suka kutsa jihar ranar Talata tare da kashe sama da mutum 100, da harin karamar hukumar Faskari a jihar Katsina wanda ya hallaka aƙalla mutum 20, sai kuma wani hari na daban a karamar hukumar Kwande na jihar Benue da ya janyo mutuwar mutane da dama.

Cikin wata sanarwa, shugaban ƙungiyar gwamnonin arewa kuma gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahaya ya nuna kaɗuwarsa kan rayukan da aka rasa, inda ya miƙa ta'aziyya a madadin sauraran gwamnonin zuwa ga iyalan waɗanda lamarin ya shafa da kuma al'ummar jihohin uku.

"Wannan ɗayen aiki abin Alla-wadai ne kuma abu ne da ba za mu lamunta ba.

"Cigaba da far wa mutane, ciki har da mata da yara da kuma tsofaffi yana ƙara nuna rashin imani na waɗannan mahara da kuma buƙatar ɗaukar mataki mai tsauri a kansu," in ji Inuwa Yahaya.

Ya yaba wa gwamnonin jihohin bisa jajircewarsu wajen ganin an daƙile barazanar tsaro da kuma tabbatar da zaman lafiya.

Gwamnan na Gombe ya shawarci jami'an tsaro da su ci gaba da hoɓɓasa da tattara bayanan sirri wajen ganin an bi sawun ƴanbindigar da nufin kama su.

Ƙungiyar gwamnonin arewar ta yi addu'ar Allah ya gafartawa waɗanda suka mutu da kuma addu'ar samun lafiya ga mutanen da suka jikkata a hare-haren.

Andrew Rau

ARE a simpleton.' Alice did not feel encouraged to ask them what the next question is, what did.