Kafofin yaɗa labaran Iran sun ce dakarun juyin juya-hali sun ƙwace jiragen ruwa biyu ɗauke da ɗanyen mai tare da ma'aikatansu a yankin Gulf.
Kamfanin dillancin labarai na Tasnim (wanda ke kusa da dakarun) ya ce jiragen ruwan na ɗauke da litocin fetur sama da miliyan ɗaya, wanda Tehran ta yi zargin cewa safarar shi a aka yi.
An kama jiragen ne bayan wani samame da aka gudanar.
Ba a dai san tutocin ƙasashen da ke jikin jiragen ba da kuma inda ma'aikatan suka fito, sai dai an damka su hannun hukumomin shari'ar Iran.
An ƙwace jiragen ne kusa da tsibirin Farsi na Iran, wanda yake kusa da Saudiyya.
Ana ci gaba da zaman ɗar-ɗar tsakanin Iran da Amurka, sai dai ƙasashen biyu na sa ran tattaunawa a ranar Juma'a.